Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya bayyana yadda tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi a matsayin mutumin da ya kubutar da shi daga tsare wajen jami’an tsaro na farin kaya (DSS) karo na biyu.
El-Rufai yayin da yake magana a ziyarar Amaechi jihar Kaduna, ya ce, matarsa ba za ta taba mantawa da abin da Amaechi ya yi na ceto shi daga hannun ‘yan sandan sirri ba.
Amaechi ya ziyarci jihar ne a ranar Lahadin da ta gabata domin neman goyon bayan wakilan jam’iyyar All Progressives Congress gabanin zaben fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar.
Gwamnan jihar Kaduna ya bayyana yadda Amaechi ya tuka shi zuwa ofishin hukumar DSS tare da tabbatar da cewa an sake shi a ranar.
El-Rufai a cikin sanarwar ya ce, “Wata lokaci jami’an SSS sun so kama ni, sai na rubuta wani abu.
“Gwamna Amaechi ya kira ya ce zan kai ka can kuma ba zan tafi ba sai sun sake ka, me ka yi?
“Ya kai ni can a cikin motarsa ya zauna har sai da suka bar ni. Har gobe matata bazata taba mantawa da hakan ba. Amaechi shine dan Najeriya da ta fi so.”
Amaechi dai zai yi fatan samun tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyya mai mulki a gaban jagoran jam’iyyar na kasa, Bola Tinubu, mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo, da sauran su.