fidelitybank

Al’ummar Neja za su rabauta da kwasha-kwashan kayan abinci a Azumin bana

Date:

Gwamnan jihar, Mohammed Umar Bago ya bayyana aniyar gwamnatinsa na bayar da tallafi domin rage farashin kayan abinci a lokacin watan ramadan.

Bago ya bayyana hakan ne a lokacin da wakilan gidauniyar Gates suka kai masa ziyara a fadar gwamnatin jihar da ke Minna, kamar yadda sakataren yaɗa labaran gwamnan, Bologi Ibrahim ya bayyana cikin sanarwar da ya fitar.

Gwamnan ya ce matakin zai kawo wa al’ummar jihar sauƙin sayen kayan abinci a lokacin azumin.

Umar Bago ya ƙara da cewa gwamnatin jihar ta noma tan miliyan guda na masara, yana mai cewa ta hanyar abincin da jihar ta noma ya taimaka wajen daidai farashin kayan abinci a faɗin ƙasar.

Hakazalika ya jaddada buƙatar samun haɗin kan gidauniyar Gates ta fuskar noman rani wanda ya bayyana a matsayin sana’ar da za ta iya amfanar da al’umma da magance sauyin yanayi.

Jagoran ayyukan noma na gidauniyar Gates, Obai Khalifa ya ce tun kafuwar gidauniyar, shekara 25 da suka gabata, ta himmatu wajen gina rayuwar al’umma.

Mista Khalifa ya bayyana noma a matsayin muhimmin abu ba kawai a mahangar tsaro ba, har ma da samar da abinci mai gina jiki.

latest news nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp