An umarci masu unguwanni a garin Ketare da ke karamar hukumar Kankara ta jihar Katsina da su tabbatar da cewa, duk wadanda suka cancanta a yankinsu sun yi rajista tare da karbar katin zabe na dindindin (PVCs).
Hakimin Ketare, Alhaji Usman Bello ne ya bada wannan umarni a lokacin da jamiāin zabe na karamar hukumar Kankara Malam Yunusa Abdu ya kai ziyarar ban girma a fadar sa.
Ya yi kira ga alāummar yankin da su yi amfani da karin waāadin da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta yi na yin rajista da kuma karbar katin zabe kafin zaben 2023 mai zuwa.
Hakimin, wanda kuma shi ne Kanwan Katsina, ya jaddada mahimmancin katin zabe na PVC, inda ya ce hakki ne da tsarin mulki ya ba duk wani dan kasa da ya cancanta ya yi amfani da ikonsa.
Tun da farko, jamiāin zabe na INEC, Malam Abdu ya ce, sun kai ziyarar ne domin sanar da hakimin gundumar cewa, hedkwatar jihar ta samar da karin naāurar rajista.
A cewarsa, karin naāurar ita ce ta rage cunkoso a wasu sassan da kuma tabbatar da an yiwa duk wadanda suka cancanta rajista a yankin.