fidelitybank

Al’umma sun koka a kan kisan gillar sojojin Anambra

Date:

Wani bidiyo da aka yada a shafukan sada zumunta, yana nuna gawawwakin sojojin da aka ba da rahoton cewa, ‘yan bindiga ne suka harbe su a kudu maso gabashin Najeriya ya janyo bacin rai a kasar.

Bidiyon maras dadin gani wanda ga alama an dauke shi ne bayan harin da aka kai ya nuna mutane zagaye da wani abu mai kama da motar jami’an tsaro an dambara rubutun “Sojoji” a kowanne bangare.

An ga gawawwaki guda biyu kwance shame-shame a kasa, sai kuma gawa biyu a mota male-male da jini.

Ba a tabbatar da kafar da ta fara yada bidiyon ba zuwa yanzu.

Rundunar soji da ta ‘yan sanda ba su fitar da wata sanarwa ba game da lamarin.

Sai dai gwamnan jihar Anambra ya yi alla-wadai da harin a kan sojoji.

Mutane sun bayyana damuwa da takaici a kan karuwar hare-haren da akasari ake far wa hukumomin tsaro da jami’an gwamnati da cibiyoyin hukuma.

Kafofin yada labarai sun ruwaito cewa ‘yan bindiga sun kashe sojoji guda hudu da kuma wani farar hula a lokacin harin na ranar Laraba a jihar Anambra ta kudu maso gabas.

legit news 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp