Gwamnatin jihar Borno ta buƙaci al’umma su kaucewa tsallake iyakokin da sojoji suka shata don kaucewa faɗawa tarkon ƙungiyar Boko Haram.
Gwamantin dai ta yin ƙarin bayani ne bayan wani hari da ƴan boko haram suka kai A ranar Lahadi, kan masunta da manoma a wani ƙauye da ke Baga a ƙaramar hukumar Kukawa.
Kwamishinan yaɗa labaran jihar ta Borno Usman Tar ya shaidawa BBC cewar manoman sun faɗa tarkon maharan ne lokacin da suka tsallake yankunan da ke da tsaro, zuwa yankunan da babu tsaro.
Ya ce tsallake iyakar ne ya ba maharan damar kai musu farmaki.