Wata kungiya mai fafutukar kawo sauyi a makarantun Tsangaya, Khalifa Dankadai Charity (KDC), ta bullo da wani shiri na karfafawa dalibai 6,000 na makarantun kur’ani da ba na boko mai suna almajiri a jihohi shida na kasar nan.
Jami’in kula da ayyukan na kungiyar, Khalifa Dankadai ne ya bayyana hakan a lokacin buda baki da masu ruwa da tsaki a harkar zamantakewa a Kano.
Ya ce, an tsara tsarin karatun ne, domin gyara tsarin makarantar Tsangaya a jihohin Katsina, Kano, Niger, Jigawa, Zamfara da Sokoto.
A cewar Dankadai, shirin zai gudana ne a makarantu 60 dake fadin yankin, kuma dalibai 1,000 ne za su ci gajiyar shirin a kowace jahohin da za su halarci taron.
Ya ce, “Manhajar ita ce a samar da ingantacciyar tsarin ilmantarwa, hade-hade da kuma basira ta hanyar aikin dakin karatu na al’umma, wanda ake aiwatarwa tare da hadin gwiwar gwamnatin Najeriya.
“Haɗin gwiwar yana tsakanin majalisun tarayya, jihohi da ƙananan hukumomi da masu ruwa da tsaki tare da tallafin ofishin jakadancin Amurka a Abuja.”
Dankadai ya ci gaba da cewa hadakar masu ruwa da tsakin ita ce yin mu’amala da masu tasiri a shafukan sada zumunta da kuma samar da hanyoyin da za a inganta harkar wayar da kan jama’a, domin hanzarta bin diddigin gyara tsarin karatun almajirai.