fidelitybank

Allurar rigakafin kyandar Biri ta sauka a Abuja

Date:

Sunƙin farko ɗauke da allurar rigakafin cutar ƙyandar biri guda dubu 10 ya isa Abuja, babban birnin Najeriya a ranar Talata.

Amurka ce dai ta bayar da tallafin allurar rigakafin da kamfanin ƙasar Denmark, Bavarian Nordic ya samar da manufar daƙile nau’in cutar ƙyandar birin ta Clade II, wadda ƙwayar cuta ce da ba ta illa sosai wadda kuma ita ce take yaɗuwa a ƙasar tun shekarar 2017, kamar yadda BBC ta rawaito.

Najeriya dai ta samu mutum fiye da 700 da ake zargin sun kamu da cutar ta kyandar biri inda aka tabbatar da kamuwar mutum 40, duk da cewa ƙwayar cutar da ta kama dukkanninsu ba mai zafi ba ce.

Cutar ta yaɗu zuwa jihohi 13 a Najeriya da suka haɗa da jihohin Bayelsa da Cross River da Ogun da Legas inda nan ne cutar ta fi shafa.

Najeriya ta ce za ta bai wa jami’an lafiya da garuruwan da ke fuskantar haɗarin kamuwa da cutar fifiko wajen allurar rigakafin.

Cibiyar da ke daƙile cutuka masu yaɗuwa a Afirka ta CDD ta yi ƙiyasin cewa ana buƙatar allurar guda miliyan 10 a nahiyar.

Jamhuriyar Dimokradiyyar Congo ce ƙasar da nau’in cutar mai zafi na Clade 1b ya fi yi wa illa a nahiyar.

Tun dai watan Janairun 2023 ne jamhuriyar ta Dimokraɗiyar Congo ta ayyana ɓullar cutar inda mutum dubu 27 suka kamu sannan fiye da 1000 suka mutu.

labaran duniya na yau

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp