fidelitybank

Allah wadarai da halin yunwa da talauci da ake fama da shi a Najeriya – CISLAC

Date:

Da yake tsokaci kan turmutsitsin da yayi sanadiyyar mutuwar mutane da dama yayin rabon kayan tallafi a sassa daban-daban na kasar, Rafsanjani ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici wanda ya nuna irin mawuyacin hali da al’ummar Najeriya ke ciki.

“Wannan yana nuna cewa ‘yan Najeriya suna fama da mawuyacin hali a karkashin wannan gwamnati,” in ji shi. “Abin takaici, gwamnati ta gaza daukar matakan da suka dace don magance matsalar da ita kanta ta kara tabarbarawa.”

Rahotanni na cewa a Abuja, turmutsutsun yayin rabon kayan abinci a Cocin Katolika ta Holy Trinity da ke Maitama ta yi sanadiyyar mutuwar mutane 10, ciki har da yara hudu, tare da jikkata wasu da dama. Shaidu sun bayyana cewa cunkoson fiye da mutum dubu daya ya haifar da lamarin a safiyar Asabar.

Haka zalika, a Okija, Jihar Anambra, rabon shinkafa da wani hamshakin dan kasuwa, Cif Ernest Obiejesi, ya shirya ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 12 tare da jikkata wasu fiye da 30. Rahotanni sun bayyana cewa cunkoson jama’a ya haddasa turereniyar kafin a fara rabon kayan.

A Ibadan, Jihar Oyo, wata liyafar yara da kungiyar Women in Need of Governance and Support (WINGS) ta shirya karkashin jagorancin Sarauniya Naomi Silekunola, ta rikide bayan cunkoson jama’a ya haddasa turereniya. Yara da dama sun rasa rayukansu, yayin da wasu suka jikkata yayin kokarin shiga wurin taron.

Rafsanjani ya bayyana wadannan lamuran a matsayin abin da za a iya kaucewa idan gwamnati ta yi aiki tuƙuru don magance matsalolin talauci da yunwa.

“Dole ne gwamnati ta dauki matakai cikin gaggawa don magance rashin abinci, samar da ayyukan yi, da rage wahalhalun jama’a,” in ji shi.

Ya kuma jaddada cewa matsalar tsaro a kasar na taimakawa wajen tabarbarewar lamarin, inda ya ce rashin tsaro ya hana manoma yin noma, wanda ke rage samar da abinci. Ya yi kira ga gwamnatin Tinubu da ta mayar da hankali kan samar da tsaro da bunkasa bangaren noma, tare da jan hankalin gwamnatocin jihohi da na kananan hukumomi su kara kokarin karfafa harkokin noma don rage zaman kashe wando da hijirar kauye zuwa birni.

current eggon news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp