Yarima Mohammed bin Salman na Saudiyya ya yi Allah-wadai da Isra’ila tare da ɗora mata alhakin abin da ya kira “laifukan da ake tafkawa a kan Falasɗinawa.”
Yariman ya kuma yi kira da a kawo ƙarshen mamayar da aka yi wa Zirin Gaza tare da samar da ƙasar Falasɗinawa bisa yarjejeniyar 1967.
Sarki Abdallah II na Jordan da kuma shugaban Falasɗinawa duk sun amince da batun na yariman na Saudiyya.
Shi kuwa shugaban Turkiyya, Raceb Tayyib Erdogan ya yi kakkausar suka ne a kan Isra’ila, tare da bayyana ta a matsayin sangartacciyar ƙasa.
Ya yi kira ga ƙasashe da su fito fili su yi magana kan rashin abin da ke faruwa a Gaza, da kuma buƙatar Isra’ila ta biya diyya ga Falasɗinawa.
Haka nan ya buƙaci a hukunta Isra’ila kan laifukan da ta aikata kan Falasɗinawa.