Ƙungiyar haɗin kan ƙasashen Musulmi, OIC ta yi Allah wadai da farmakin da sojojin Isra’ila suka kai da ya raunata Falasdinawa 150 a Masallacin Al Aqsa a birnin Kudus.
Shelƙwatar ƙungiyar da ke Saudiyya ta yi Allah wadai da abin da ta kira “barazana mai hatsari” daga sojojin Isra’ila a wuri mai tsarki.
Ƙungiyar ta ce, wannan tashin hankalin wani hari ne da ya shafi tunanin al’ummar musulmi baki ɗaya da kuma keta dokokin kasa da kasa.
Gwamnatin Saudiyya ba ta ce komi ba zuwa yanzu game da al’amarin.
Rikicin na zuwa a yayin kisan Falasɗinawa ke ƙaruwa a fito na fiton da suke yi da sojojin Isra’ila a Gaɓar Yamma da Kogin Jordan, da kuma hare-haren da ƴan bindiga daga ɓangaren Falasdinawa ke kai wa a Isra’ila.