fidelitybank

Allah ne ya zabi Atiku ya mulki Najeriya – Ayu

Date:

Shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Dr. Iyorchia Ayu, ya yi ikirarin cewa, Allah ya zabi tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar a matsayin shugaban kasar Najeriya.

Ayu ya ce Allah ne ya zabi Atiku a matsayin shugaban Najeriya domin ya magance kalubalen da ke addabar Najeriya.

Da yake jawabi jiya a Bauchi yayin da yake karbar dubban masu sauya sheka, Ayu ya ce Allah ne ya zabi Atiku ya hada kan kasar nan.

Da yake lura da cewa Arewa maso Gabas ba ta taba samar da shugaban Najeriya ba, Ayu ya ce: “Amma a yau, Allah ya zabi Atiku Abubakar, wanda dan Arewa maso Gabas ne, domin ya gyara duk wani kalubalen da ke dagula al’ummar kasa da kuma hada kan ta.”

Ya kuma tabbatar wa da wadanda suka sauya sheka cewa za su ji dadin fage a cikin jam’iyyar PDP.

Ya kuma bayyana cewa masu kokarin kawo rarrabuwar kawuna a jam’iyyar za su ji takaici.

“Akwai makiyan jam’iyyar da suka kuduri aniyar haifar da rarrabuwar kawuna a tsakaninmu ta hanyar yi mana karya iri-iri. Ina so in gaya muku cewa za su ji kunya domin a karshen ranar ’yan jam’iyyar za su fito gaba daya su kada kuri’a.

“Dukkan majalissar mu ta kasa, ‘yan takarar gwamna za su dawo ofis. Da ya yi shekara takwas ba ta mulki, PDP za ta dawo mulki,” inji shi.

Wasu jiga-jigan jam’iyyar PDP sun yi ta kiraye-kirayen a tsige Ayu sakamakon fitowar Atiku a matsayin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar.

Gwamnan jihar Ribas, Nyesome Wike ne ya jagoranci kiran a tsige Ayu.

Wike ya bayar da hujjar cewa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP da shugaban kasa ba za su iya fitowa daga yanki daya ba.

opra news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Peter Obi na nan a cikin jam’iyyar har yanzu – LP

Shugaban Ĉ™ungiyar Obidient Movement, Dr. Tanko Yunusa ya ce...

Yadda Mahara sun kashe mutum biyu, sun Ĉ™ona gidaje a Filato

Wasu da ake zargin mahara sun afka wa karamar...

An YI zanga-zanga a Isra’ila kan shirin Netanyahu na mamaye Gaza

Dubban mutane sun fito kan tituna a faɗin Isra'ila,...

Birtaniya za ta fara tisa Ĉ™eyar bakin da suka aikata laifi zuwa kasarsu

Birtaniya ta fitar da sabon tsarin tisa keyar duk...

NDLEA ta kama Fasto kan zargin safarar miyagun Ĉ™wayoyi

Hukumar hana sha da fataucin miyagun Ĉ™wayoyi ta Najeriya,...

Gwamnoni sun mika sakon ta’azziya ga iyalan Audu Ogbeh

Shugaban Ĉ™ungiyar gwamnonin arewa kuma gwamnan jihar Gombe, Muhammadu...

Duk wahala sai dai mu mutu a Gaza – Fatma

Wata mai mai Ĉ´aĈ´a tara ta ce, duk runtsi...

Gwamnan Kano ya kori mataimansa na musamman kan belin Danwawu

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da...

Tsohon Minista a mulkin Buhari ya mutu

Allah ya yi wa tsohon ministan noma da raya...

Kashi 70 na yankin Bukuyum ta Kudu na Ĉ™arĈ™ashin Ĉ´an Bindiga – ĈŠan majalisa

Rahotanni daga yakin Ĉ™aramar hukummar Bukuyum na jihar Zamfara...

Goodluck ya fi dacewa ya zama dan takara a 2027 – Lamido

Tsohon Gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido ya ce Tsohon...

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...
X whatsapp