fidelitybank

Alkalai APC su ke yi wa aiki ƙiri-ƙiri – Atiku

Date:

Jagoran adawa a Najeriya ya yi zargin cewa manufar jam’iyya mai mulkin kasar wato APC, ta kwacen mulkin jam’iyyun adawa, babban naƙasu ne ga tsarin dimokraɗiyya.

Atiku Abubakar ya ce abin takaici ne yadda kwatsam suke ganin wani salo, inda jam’iyya mai mulki ke ci gaba da dakushe ƙoƙarin damawa da jam’iyyun adawa a harkokin mulkin Najeriya.

“Ko dai ta hanyar zabe, inda ake yi wa jam’iyyun adawa maguɗi ƙuru-ƙuru cike da galatsi, ko kuma a kotuna inda ɓangaren shari’a ke yi wa jam’iyyar APC mai mulki aiki,” in ji shi.

“A bayyane take dimokradiyyar Najeriya tana ƙara shiga halin rashin lafiya.”

Sai dai wani alkali a daya daga cikin hukunce-hukuncen da aka yanke wadanda ba su yi wa ‘yan adawa dadi ba, ya zargi jam’iyyu da sakaci da kuma ƙin aiki da doka wajen fitar da ‘yan takara a zabukansu na fitar da gwani, daga bisani kuma su je suna zargin kotuna da alkalai da rashin adalci.

Atiku ya ce “azancin mulkin dimokradiyya bai tsaya kawai a kan gwamnati mai wakilcin jama’a ba kawai, ginshikinta ya samo asali ne daga akidun jam’un mutane”.

A cewarsa, kafin duk wani tsari ya amsa sunan dimokradiyya ta gaskiya, jazaman ne sai an shigar da ‘yan adawa da kuma ra’ayoyin ‘yan adawa.

guardian newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp