fidelitybank

Alkalai APC su ke yi wa aiki ƙiri-ƙiri – Atiku

Date:

Jagoran adawa a Najeriya ya yi zargin cewa manufar jam’iyya mai mulkin kasar wato APC, ta kwacen mulkin jam’iyyun adawa, babban naƙasu ne ga tsarin dimokraɗiyya.

Atiku Abubakar ya ce abin takaici ne yadda kwatsam suke ganin wani salo, inda jam’iyya mai mulki ke ci gaba da dakushe ƙoƙarin damawa da jam’iyyun adawa a harkokin mulkin Najeriya.

“Ko dai ta hanyar zabe, inda ake yi wa jam’iyyun adawa maguɗi ƙuru-ƙuru cike da galatsi, ko kuma a kotuna inda ɓangaren shari’a ke yi wa jam’iyyar APC mai mulki aiki,” in ji shi.

“A bayyane take dimokradiyyar Najeriya tana ƙara shiga halin rashin lafiya.”

Sai dai wani alkali a daya daga cikin hukunce-hukuncen da aka yanke wadanda ba su yi wa ‘yan adawa dadi ba, ya zargi jam’iyyu da sakaci da kuma ƙin aiki da doka wajen fitar da ‘yan takara a zabukansu na fitar da gwani, daga bisani kuma su je suna zargin kotuna da alkalai da rashin adalci.

Atiku ya ce “azancin mulkin dimokradiyya bai tsaya kawai a kan gwamnati mai wakilcin jama’a ba kawai, ginshikinta ya samo asali ne daga akidun jam’un mutane”.

A cewarsa, kafin duk wani tsari ya amsa sunan dimokradiyya ta gaskiya, jazaman ne sai an shigar da ‘yan adawa da kuma ra’ayoyin ‘yan adawa.

vgn news today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp