fidelitybank

Aljeriya za ta sasanta rikicin Nijar da ECOWAS

Date:

Babban jami’in diflomasiyyar Aljeriya ya fara wata ziyarar aiki zuwa kasashen yammacin Afirka ranar Laraba a wani yunkuri na neman mafita bayan juyin mulkin da aka yi a makwabciyarta Nijar

Aljeriya ba ta goyon bayan duk wani matakin soji a Nijra.

Shugaban ƙasar Abdelmadjid Tebboune ya buƙaci ministan harkokin wajen ƙasar Ahmed Attaf ya je Najeriya da Benin da Ghana domin tattaunawa da mahukuntan ƙasashen, kamar yadda ma’aikatar harkokin wajen Aljeriya ta wallafa a shafinta na X.

Ecowas ta ce watakila za ta yi amfani da karfin soji wajen mayar da hamɓararren shugaban ƙasar Nijar, Mohamed Bazoum, wanda sojojin ƙasar ke tsare da shi tun ranar 26 ga watan Yuli.

Aljeriya mai iyaka da Nijar ta ce yin amfani da karfin sojoji ba zai magance matsalar ba, inda shugaba Tebboune ya ce hakan zai cutar da Aljeriya kai tsaye.

Shugaban ƙasar ya yi imanin cewa Aljeriya ce ta farko da lamarin juyin mulkin Nijar din ya shafa.

A ranar Talata ƙungiyar Tarayyar Afirka ta dakatar da Nijar har sai an sake samun gwamnatin farar hula.

Aljeriya ce kasa mafi girma a Afirka kuma tana kan iyaka da Libya da Mali, dukkansu suna fuskantar rikici tsawon shekaru.

latest news 
in nigeria today 2021 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp