Shahararren jarumin fina-finan nan, Ali Nuhu, ya caccaki Davido kan faifan bidiyo mai cike da ce-ce-ku-ce na mawakin, Logos Olori na sabuwar wakar mai suna ‘Jaye Lo.
Davido ya janyo cece-kuce bayan fitar da wani gajeren faifan bidiyon wakar da ya dauki mutane suna Sallah wasu na rawa a gaban wani masallaci, a shafin Twitter.
Da yake mayar da martani ta shafinsa na Instagram, Ali Nuhu ya ce aikin da aka bayyana a bidiyon “ba abu ne da Musulunci ya amince da shi ba.”
Jarumin ya bukaci Davido da ya cire faifan bidiyon kuma ya nemi gafarar Musulmai saboda “rauni” da suka yi.
Ya rubuta cewa, “Na ci karo da faifan bidiyo mai cike da cece-kuce da @davido ya yi, kasancewar muna son yin kirkire-kirkire a fannonin mu daban-daban, ya kamata mu koyi mutunta addini da al’adar wasu.
“Wannan sam ba abin yarda ba ne a Musulunci. Ku cire wannan bidiyon ku bada hakuri kan cutar da al’ummar musulmi baki daya.”