fidelitybank

Alhini: Korea ta Arewa ta haramta yin Dariya da Cefane na tsawon kwanaki 11

Date:

Kasar Koriya ta Arewa ta haramta yin dariya ga ’yan kasarta, musamman ma a wajen shan Giya ko yin duk wani abu da ke nuna farin ciki na tsawon kwana 11.

An dauki matakin ne domin bikin cika shekara 11 da rasuwar tsohon shugaban Kasar, Kim Jong na II.

Hukumomin kasar Koriya ce ta bayar da wannan umarnin dokar, domin nuna alhinin mutuwar tsohon shugaban, wanda ya mulki kasar tsakanin shekarar 1994 zuwa 2011.

Bayan rasuwarsa ne dai shugaba mai ci, Kim Jong Un, wanda shi ne na Uku a cikin kananan ’ya’yansa, ya karbi ragamar mulkin kasar.

Wani dan kasar mazaunin birnin Sinuiju, ya shaida wa gidan rediyon Free Asia cewa, “A iya tsawon lokacin alhinin, ba mu da ikon shan Giya, yin dariya ko aikata duk wani abin jin dadi. A baya, duk wadanda a ka taba kamawa sun karya dokar, an yanke musu hukunci a matsayin masu aikata babban laifi, inda a ka batar da su, babu wanda ya kara jin duriyar su ko kuma labarinsu”.

Ya ci gaba da cewa, “Ko da wani a danginku ya mutu, ba ka da ikon yin kuka da karfi, kuma ba za a fitar da gawarsa ba sai wa’adin kwanakin ya cika. Ko bikin murnar zagayowar ranar haihuwa ba za a yi ba tsawon lokacin,” inji Sinuiju.

Majiyar ta kara da cewa, an kuma haramta wa ’yan kasar yin cefane dungurungum a ranar 17 ga watan Disamba, wacce ita ce ainihin ranar da tsohon shugaban ya rasu. Inji Aminiya.

legitnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp