fidelitybank

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Date:

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar rukunin farko na alhazan Najeriya da suka yi aikin Hajjin shekarar 2025 a kasar Saudiyya.

Jimillar maniyyata 1,310 ne suka dawo kasar ta jiragen sama guda hudu daga Jeddah na kasar Saudiyya, a cewar wata sanarwa da babban jami’in yada labarai na NAHCON, Shafii Mohammed ya fitar.

Ya ce, “Jirgin Maxair VM269 ya tashi daga Jeddah zuwa Bauchi da karfe 08:07 na safe da alhazai 551 da jami’ai bakwai. Jirgin Flynas XY9006 ya tashi daga Jeddah zuwa Kebbi da karfe 09:45 na safe da alhazan Kebbi 413 da jami’ai shida.”

Sanarwar ta kuma bayyana cewa, kamfanonin jiragen sama na UMZA da Air Peace na cikin rukunin farko na dawo da jiragen.

“Jirgin UMZA mai suna UY3534 ya tashi daga Jeddah zuwa Abuja da karfe 13:12 tare da alhazai 41 da jami’ai 122, yayin da jirgin Air Peace APK7901 ya tashi daga Jeddah zuwa Owerri da karfe 23:45 na safe tare da alhazai 305 da jami’ai bakwai,” ya kara da cewa.

NAHCON ta ce kimanin alhazan Najeriya 63,000 ne suka halarci aikin Hajjin shekarar 2025 da aka kammala.

Hukumar ta bayar da tabbacin cewa za a hada kai a tsanake domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali ga mahajjatan.

nigerianewspapers.com.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...

Ba za mu jingine yajin aiki ba har sai an biya mana buƙatun mu – Ma’aikatan Jinya

Shugaban ƙungiyar ma'aikatan jinya ta Najeriya, Morakinyo-Olajide Rilwan ya...

Za a fara yi wa Dalibai gwajin kwaya kafin su shiga jami’a – NDLEA

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta fara yi wa...

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...
X whatsapp