Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar rukunin farko na alhazan Najeriya da suka yi aikin Hajjin shekarar 2025 a kasar Saudiyya.
Jimillar maniyyata 1,310 ne suka dawo kasar ta jiragen sama guda hudu daga Jeddah na kasar Saudiyya, a cewar wata sanarwa da babban jami’in yada labarai na NAHCON, Shafii Mohammed ya fitar.
Ya ce, “Jirgin Maxair VM269 ya tashi daga Jeddah zuwa Bauchi da karfe 08:07 na safe da alhazai 551 da jami’ai bakwai. Jirgin Flynas XY9006 ya tashi daga Jeddah zuwa Kebbi da karfe 09:45 na safe da alhazan Kebbi 413 da jami’ai shida.”
Sanarwar ta kuma bayyana cewa, kamfanonin jiragen sama na UMZA da Air Peace na cikin rukunin farko na dawo da jiragen.
“Jirgin UMZA mai suna UY3534 ya tashi daga Jeddah zuwa Abuja da karfe 13:12 tare da alhazai 41 da jami’ai 122, yayin da jirgin Air Peace APK7901 ya tashi daga Jeddah zuwa Owerri da karfe 23:45 na safe tare da alhazai 305 da jami’ai bakwai,” ya kara da cewa.
NAHCON ta ce kimanin alhazan Najeriya 63,000 ne suka halarci aikin Hajjin shekarar 2025 da aka kammala.
Hukumar ta bayar da tabbacin cewa za a hada kai a tsanake domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali ga mahajjatan.