fidelitybank

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Date:

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar rukunin farko na alhazan Najeriya da suka yi aikin Hajjin shekarar 2025 a kasar Saudiyya.

Jimillar maniyyata 1,310 ne suka dawo kasar ta jiragen sama guda hudu daga Jeddah na kasar Saudiyya, a cewar wata sanarwa da babban jami’in yada labarai na NAHCON, Shafii Mohammed ya fitar.

Ya ce, “Jirgin Maxair VM269 ya tashi daga Jeddah zuwa Bauchi da karfe 08:07 na safe da alhazai 551 da jami’ai bakwai. Jirgin Flynas XY9006 ya tashi daga Jeddah zuwa Kebbi da karfe 09:45 na safe da alhazan Kebbi 413 da jami’ai shida.”

Sanarwar ta kuma bayyana cewa, kamfanonin jiragen sama na UMZA da Air Peace na cikin rukunin farko na dawo da jiragen.

“Jirgin UMZA mai suna UY3534 ya tashi daga Jeddah zuwa Abuja da karfe 13:12 tare da alhazai 41 da jami’ai 122, yayin da jirgin Air Peace APK7901 ya tashi daga Jeddah zuwa Owerri da karfe 23:45 na safe tare da alhazai 305 da jami’ai bakwai,” ya kara da cewa.

NAHCON ta ce kimanin alhazan Najeriya 63,000 ne suka halarci aikin Hajjin shekarar 2025 da aka kammala.

Hukumar ta bayar da tabbacin cewa za a hada kai a tsanake domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali ga mahajjatan.

tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp