fidelitybank

Alhazan Najeriya 15 ne suka rasu yayin aikin hajjin bana

Date:

Hukumar kula da alhazai ta kasa NAHCON, tabbatar da rasuwar alhazanta 15 daga cikin alhazan nata fiye da dubu 50 da suka yi aikin hajjin bana da aka kammala a Saudiyya.

Hukumar Alhazan ƙasar ce ta tabbatar da hakan a yayin taron manema labarai da ta gudanar na bayan kammala Arfa, a Makkah.

A ranar Laraba ne aka kammala aikin Hajjin na bana a hukumance, wanda ya ƙare cikin alhini sakamakon mutuwar ɗaruruwan alhazai.

Saudiyya ba ta bayyana adadin alhazan da suka mutu ba a hukumance, kodayake hukumomi sun ce an kai rahoton sama da mutum 2,700 da suka yi fama da bugun zafi a ranar Lahadi kaɗai.

Sai dai a cewar kamfanin labarai na AFP bayan tattara bayanai daga ofisoshin jakadancin ƙasashe, aƙalla alhazai 922 ne suka mutu yayin aikin Hajjin akasari saboda tsananin zafi da aka yi fama da shi.

Sama da mutum miliyan 1 da dubu 800 ne suka gudanar da aikin Hajji na bana, kuma miliyan 1 da dubu 600 cikinsu baƙi ne ‘yan ƙasar waje, kamar yadda mahukuntan Saudiyya suka bayyana.

Ibadar Hajji ɗaya ce cikin rukunnan Musulunci biyar, kuma ana son duk wani Musulmi da ya samu dama ya je ɗakin Ka’aba mai tsarki don yinta sau ɗaya a rayuwarsa.

legitnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp