fidelitybank

Alhazan jihar Kebbi 430 sun dawo gida

Date:

Wasu maniyyata 430 daga jihar Kebbi da suka gudanar da aikin hajjin bana a birnin Makkah na kasar Saudiyya sun dawo Najeriya.

Da safiyar yau Litinin ne alhazan suka isa filin jirgin saman Sir Ahmadu Bello International Airport Birnin Kebbi.

An ce jirgin AIRBUS A330 ya taso ne daga filin jirgin sama na Jeddah na kasar Saudiyya da misalin karfe 9 na dare agogon Saudiyya ya sauka a Najeriya karfe 1:20 na safe.

Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan Jihar Kebbi, Ahmed Idris, ya tabbatar da isar Alhazan cikin nasara a wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin.

Idris ya ce jirgin ya yi jigilar maniyyata ne daga kananan hukumomin Argungu da Dandi na jihar, da kuma wasu jami’an gwamnatin Kebbi.

A cewarsa, a daren Lahadi ne ake sa ran jirgin na uku zai tashi daga kasar Saudiyya zuwa Najeriya da safiyar Litinin mai zuwa.

A baya Saudiyya ta sanar da cewa mahajjata 1,301 ne suka mutu a aikin hajjin bana.

A wata hira da manema labarai, ministan lafiya na kasar, Fahd Al-Jalajel, ya ce kashi 83 cikin 100 na mace-macen mutane 1,301 alhazai ne ba tare da izini ba, wadanda suka yi tafiya mai nisa cikin tsananin zafi don gudanar da aikin hajji.

Ministan ya ce mahajjata 95 na jinya a asibitoci, wasu daga cikinsu an dauke su ta jirgin sama domin yi musu magani a Riyadh babban birnin kasar Saudiyya.

“Mutane 1,301 sun mutu a lokacin aikin Hajji1445. Allah ya jikan su baki daya, kashi 83% nasu ba su da izinin zuwa aikin Hajji, wadanda suka yi tafiya mai nisa a karkashin rana, ba tare da matsuguni ba, ba su huta ba, ciki har da dimbin tsofaffi da masu fama da cututtuka.” Inji shi.

latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp