fidelitybank

Alhazan bogi sun yi mana kutse – NAHCON

Date:

Hukumar alhazai ta kasa, NAHCON, ta bayyana damuwa a kan kutsen da alhazan bogi suka yi a Mina da Arafa wanda ya janyo rashin isassun tantuna a tsakanin mahajjatan Najeriya.

Shugaban Hukumar, Alhaji Zikrullah Hassan ne ya bayyana haka yayin wata ziyarar aiki da ya kai wa Mutawif, kamfanin kula da alhazan ƙasashen Afirka da waɗanda ba Larabawa ba, a birnin Makkah na kasar Saudiyya.

Kamfanin dillancin labaran Najeriya ya ambato Zikrullah Hassan na cewa “Da farko, zan so na mayar da martani a kan yadda alhazan bogi suka mamaye yankunan aikin Hajjin bana kuma wannan abin kunya ne.

“Ban san iyakar adadinsu ba, amma mun ga mutanen da ba su da wani aiki a Mina, bayan ‘yan kwanaki sai kuma suka mayar da Mina tamkar kasuwa ko kuma wurin biki.

“Duk da haka, ba mu da ikon bincikar su. Ba mu ne ke da ikon tsaro ba saboda haka babu yadda za mu iya tunkarar lamarin, gaskiya hakan abin kunya ne.

Hassan ya ce tantunan da aka yi amfani da su a aikin Hajjin bara wajen tsugunnar da mahajjata 43,000, su ne tantunan da Najeriya ta yi amfani da su ga mahajjata 95,000 yayin aikin hajjin bana.

“Saboda rashin isassun tantuna, yawancin mahajjata da suka yi burin gudanar da aikin Hajji cikin kwanciyar hankali da jin daɗi, sun ƙare da samun kansu cikin rana tsawon kwanaki.

“Mutane da yawa ba su san cewa mafi girman abin da za mu iya yi a matsayinmu na hukumar aikin Hajji shi ne kawai yin korafi ba. Ba mu da wani iko a kan lamarin.

legit.ng.news.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp