fidelitybank

Alhazan bogi sun yi mana kutse – NAHCON

Date:

Hukumar alhazai ta kasa, NAHCON, ta bayyana damuwa a kan kutsen da alhazan bogi suka yi a Mina da Arafa wanda ya janyo rashin isassun tantuna a tsakanin mahajjatan Najeriya.

Shugaban Hukumar, Alhaji Zikrullah Hassan ne ya bayyana haka yayin wata ziyarar aiki da ya kai wa Mutawif, kamfanin kula da alhazan ƙasashen Afirka da waɗanda ba Larabawa ba, a birnin Makkah na kasar Saudiyya.

Kamfanin dillancin labaran Najeriya ya ambato Zikrullah Hassan na cewa “Da farko, zan so na mayar da martani a kan yadda alhazan bogi suka mamaye yankunan aikin Hajjin bana kuma wannan abin kunya ne.

“Ban san iyakar adadinsu ba, amma mun ga mutanen da ba su da wani aiki a Mina, bayan ‘yan kwanaki sai kuma suka mayar da Mina tamkar kasuwa ko kuma wurin biki.

“Duk da haka, ba mu da ikon bincikar su. Ba mu ne ke da ikon tsaro ba saboda haka babu yadda za mu iya tunkarar lamarin, gaskiya hakan abin kunya ne.

Hassan ya ce tantunan da aka yi amfani da su a aikin Hajjin bara wajen tsugunnar da mahajjata 43,000, su ne tantunan da Najeriya ta yi amfani da su ga mahajjata 95,000 yayin aikin hajjin bana.

“Saboda rashin isassun tantuna, yawancin mahajjata da suka yi burin gudanar da aikin Hajji cikin kwanciyar hankali da jin daɗi, sun ƙare da samun kansu cikin rana tsawon kwanaki.

“Mutane da yawa ba su san cewa mafi girman abin da za mu iya yi a matsayinmu na hukumar aikin Hajji shi ne kawai yin korafi ba. Ba mu da wani iko a kan lamarin.

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp