A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan 1.8 suka kammala aikin Hajjin bana a birnin Makkah na kasar Saudiyya, bayan kammala jifan shaiÉ—an a Jamarat da ke Mina.
Ko da yake a shari’ance a ranar Litinin ne ranakkun aikin Hajjin shida ke cika, saboda yadda addini ya bai wa mahajjatan damar kammalawa cikin kwanaki biyar ko shida inda kuma mafi yawan alhazan ke zaÉ“ar kammalawa cikin kwana biyar É—in.
Masu son ƙarawa su ma za su kammala ne ranar Litinin da jifan shaiɗan da ake kira Jamrat a rana ta huɗu maimakon uku da dama ke yi.
Gabanin jifan Jamarat ɗin, mahajjatan sun yi hawan Arafa da kwanan Muzdalifah da Ɗawaful Ifadah da kuma Sa’ayi.