Yau ne alhazai ke fita filin Arfa a ci gaba da gudanar da ayyukan hajjin bana.
Kimanin alhazai miliyan guda ne suka fita domin tsayuwar ta arfa inda za su kwashe yinin ranar wato tun daga zawali zuwa faduwar rana suna addu’oi kafin daga bisani su wuce zuwa Musdalifa.
Ranar Arfa ita ce, rana mafi girma da muhimmnanci a duka kwanakin aikin hajji. Ko a hadisi ma ya zo, Annabi SAW yace Arfa ita ce hajji.
Don haka duk alhajin da bai shiga filin arfa ba har rana ta fadi a yau to ba shi da aikin hajji, sai ya sake.
Hakan ta sa a kowane irin hali mutum ya ke ciki sai ya je filin, hatta ma marasa lafiya ana kai su.
Hukumomin Saudiya sun yi wani tanadi na daukar marassa lafiya da ke cikin mawuyacin hali a kai su filin a cikin motocin daukar marassa lafiya, domin su dace da samun ranar.
A Arfah dai alhazai suna hada sallar Azahar da La’asar, kuma raka’a bibbiyu.
Daga nan za su zauna suna ta addu’o’I da karatun kur’ani da zikiri har zuwa faduwar rana.
Idan rana ta fadi kuma ba za su yi sallar magriba a filin Arfa ba, sai su kama hanyar tafiya Muzdalifa.