fidelitybank

Alhazai na filin Arfa a kasar Saudiyya

Date:

Yau ne alhazai ke fita filin Arfa a ci gaba da gudanar da ayyukan hajjin bana.

Kimanin alhazai miliyan guda ne suka fita domin tsayuwar ta arfa inda za su kwashe yinin ranar wato tun daga zawali zuwa faduwar rana suna addu’oi kafin daga bisani su wuce zuwa Musdalifa.

Ranar Arfa ita ce, rana mafi girma da muhimmnanci a duka kwanakin aikin hajji. Ko a hadisi ma ya zo, Annabi SAW yace Arfa ita ce hajji.

Don haka duk alhajin da bai shiga filin arfa ba har rana ta fadi a yau to ba shi da aikin hajji, sai ya sake.

Hakan ta sa a kowane irin hali mutum ya ke ciki sai ya je filin, hatta ma marasa lafiya ana kai su.

Hukumomin Saudiya sun yi wani tanadi na daukar marassa lafiya da ke cikin mawuyacin hali a kai su filin a cikin motocin daukar marassa lafiya, domin su dace da samun ranar.

A Arfah dai alhazai suna hada sallar Azahar da La’asar, kuma raka’a bibbiyu.

Daga nan za su zauna suna ta addu’o’I da karatun kur’ani da zikiri har zuwa faduwar rana.

Idan rana ta fadi kuma ba za su yi sallar magriba a filin Arfa ba, sai su kama hanyar tafiya Muzdalifa.

bbc nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp