Mataimaki na musamman ga babban sakataren hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kaduna, Ibrahim Giwa, ya tabbatar da mutuwar wasu alhazai biyu daga jihar.
Ya ce mahajjatan biyu sun rasu ne a lokacin da suke gudanar da aikin hajji a kasar Saudiyya.
A cewarsa, mahajjatan sun hada da Bashir Umar Sambo daga karamar hukumar Kubau da Sulaiman Abubakar (Unguwan Lalli) daga karamar hukumar Igabi ta jihar.
Ya bayyana cewa, “Hukumar jin dadin Alhazai ta jihar Kaduna ta sanar da rasuwar Sulaiman Abubakar Unguwan Lalli, KD 086 TRK daga karamar hukumar Igabi da Bashir Umar Sambo, KD 318 KB daga karamar hukumar Kubau.”
Alhazan biyu da suka rasu a baya-bayan nan ya kawo adadin maniyyatan da suka rasu a Saudiyya zuwa hudu daga jihar.