Shugaban masu rinjaye na majalisar Alhassan Ado-Doguwa mai wakiltar mazabar Doguwa/Tudun Wada a jihar Kano ya samu tikitin jamâiyyar All Progressives Congress ba tare da hamayya ba a zaben 2023 mai zuwa.
Ado-Doguwa, wanda ya kasance dan majalisar wakilai a rusasshiyar jamhuriya ta uku, kuma ya koma majalisar a jamhuriya ta hudu a halin yanzu, zai sake neman tsayawa takara a karo na bakwai. Ana iya cewa shi ne ya fi kowa matsayi a majalisar.
A shekarar 1992 ne aka zabe shi a majalisar inda ya kafa tarihi inda ya zama dan Najeriya na farko da aka rantsar a matsayin mamba nan take bayan ya kammala hidimar matasa ta kasa.
Wannan shi ne aiki na na 7, na tsayawa takarar Majalisar Wakilai ba tare da hamayya ba, ba tare da wata gardama ba. In ji shi.