fidelitybank

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Date:

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa yayin da Musulmai kusan miliyan biyu ke gudanar da aikin Hajji a ƙasar Saudiyya.

Shugaban Hukumar aikin hajji ta Najeriya, Abdullahi Saleh Pakistan ne ya bayyana hakan lokacin da ya tattauna da manema labarai yau Alhamis a filin na Arafa.

Saleh ya ce “mun samu labari akwai alhazanmu guda biyu waɗanda Allah ya yi musu rasuwa, ɗaya ma a nan filin Arfa Allah ya karɓi rayuwarsa, ɗaya kuma tun muna Makka.”

Sai dai shugaban na hukumar aikin hajji ta Najeriya ya ce rasuwar maniyyacin ba ya da alaƙa da tsananin zafi da ake fuskanta a ƙasar ta Saudiyya yayin aikin hajjin.

Hawan Arfa na daga cikin ginshiƙan aikin Hajji, wanda shi kansa ɗaya ne daga cikin ginshiƙan imani ga mabiya addinin Musulunci.

Rana ce da dukkanin mahajjata ke taruwa a kai da kuma kewayen dutsen Arfa domin yin addu’o’i na neman dacewa da kuma gafara, a wurin da Annabi Muhammad ya yi jawabi lokacin aikin hajjinsa na ƙarshe.

Ma’aikatar aikin hajji da Umara ta Saudiyya ta shawarci maniyyata aikin Hajjin na bana da su guje wa yawan zirga-zirga ko fita daga tantunasu tsakanin ƙarfe 10 na safe zuwa 4 na yamma domin kauce wa zafin rana.

Masana sun yi hasashen cewa yanayin zafi zai kai maki 45 a ma’auni a ranakun aikin Hajjin a garuruwan Makka da Mina.

breaking news in nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp