fidelitybank

Algeria ta dakatar da shiga tsakanin sasanta rikicin Nijar

Date:

Algeria ta bayyana dakatar da yunkurinta na shiga tsakani a rikicin siyasar Nijar bayan juyin mulkin da aka yi a watan Yuli.

Ma’aikatar harkokin wajen kasar ta sanar a cikin wata sanarwa ranar Litinin cewa, sanarwar da hukumomin Nijar suka fitar ta haifar da “halastattun tambayoyi game da ainihin aniyarsu ta amincewa da shiga tsakanin Aljeriya”.

A yanzu dai, an dakatar da wannan mataki har sai sun samu tabbataciyar magana daga shugabannin mulkin sojan Nijar a kan ci gaba da shiga tsakanin.

A watan jiya, Nijar ta amince da tayin Aljeriya na shiga tsakani a rikicin siyasarta, da nufin mayar da kasar kan tafarkin dimokradiyya.

A watan Agusta, Aljeriya ta bai wa mahukuntan Nijar shawarar mika mulki a cikin wata shida zuwa hannun gwamnatin farar hula.

Sai dai shugaban gwamnatin mulkin sojan kasar, Janar Abdourahmane Tchiani, wanda ya karbe iko a watan Yuli, ya bukaci mika mulki a cikin shekara uku.

Aljeriya ta kuma nuna rashin amincewa da matakin soji a matsayin hanyar warware rikicin Nijar bayan barazanar da kungiyar Ecowas ta yi na yiwuwar tura dakarun sojoji su mayar da mulkin dimokradiyya.

Shugaban Najeriya Bola Tinubu, wanda kuma shi ne shugaban Kungiyar raya Tattalin Arzikin Kasashen Afirka ta Yamma ya yi maraba da matakin shiga tsakanin, amma wannan sabon lamari zai kara kawo cikas ga ƙoƙarin warware rikicin siyasar Nijar.

vanguardnewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp