Firaministan Albania ya ce gwamnati za ta toshe kafar sada zumunta ta TikTok a kasar na tsawon aƙalla shekara ɗaya daga watan Janairu.
Tun lokacin da wani bidiyo ya bayyana a watan da ya gabata na kisan wani yaro ɗan shekara 14 da wani dalibi ya yi ta hanyar yi masa yankan rago ne gwamnatin kasar ta fara nazarin toshe kafar.
Karo na hudu kenan da irin wannan kisan ke faruwa a wannan shekarar, lamarin da ya haifar zazzafar muhawara.
Kamfanin TikTok ya ce zai nemi ƙarin bayani kan yunƙurin matakin daga gwamnatin Albania