fidelitybank

Al-Nasr za ta ɗauke Boniface daga Leverkusen

Date:

Rahotanni daga Jamus sun tabbatar da cewa ƙungiyar Al-Nassr, ta cimma cikakkiyar yarjejeniya da Bayer Leverkusen domin ɗaukar ɗan wasan Najeriya Victor Boniface.

Rahotannin dai na cewa albashin ɗan wasan mai shekara 24 zai iya kai wa Yuro miliyan 15 a duk kakar wasa.

Tuni dai ɗan wasan ya kammala gwajin duba ƙoshin lafiyarsa a kulob ɗin na Saudi Pro League.

Ɗan wasan ya taka rawar gani a kakar wasan da ta gabata, inda ya taimakawa Leverkusen ta lashe gasar Bundesliga, da kofin Jamus, da kuma Super Cup na Jamus,

A wannan kakar, ya buga wasanni 34, inda ya zura ƙwallaye 21 ya taimaka aka ci 10.

Rashin halartar atisayen Leverkusen da Boniface ya yi a ranar Talata ya kara rura wutar raɗe-raɗin tafiyar tasa.

Da yake magana da manema labarai, kocin Leverkusen Xabi Alonso ya amince da tattaunawar sauya sheƙar ɗan wasan da ke gudana kuma ya tabbatar da cewa shirye-shiryen ƙungiyar na wasan ƙarshe a zagayen rukuni na gasar cin kofin zakarun Turai na ci gaba da gudana ba tare da Boniface ba.

nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...
X whatsapp