Hukumar ‘yan sandan ciki ta DSS, ta ce, akwai shirin da wasu mutane ke yi na tayar da hankali a wasu sassan ƙasar nan a zaɓen gwamnoni da ke tafe.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar, Peter Afunanya ya fitar a ranar Laraba, ta gargaɗi mutane ko kungiyoyi da su guji yin duk abin da zai tayar da hankali domin kauce wa fushin hukuma.
A don haka DSS ɗin ta ja kunnen ‘yan siyasa da su zama masu bin doka da oda a daidai lokacin da ‘yan ƙasa ke shirin fita rumfunan zaɓe domin zaɓen gwamnoni da ‘yan majalisar dokoki a ranar 18 ga watan Maris.
Hukumar ta ce a shirye ta ke domin kare ‘yan ƙasar waɗanda ke da niyyar fita kaɗa kuri’a.
DSS ɗin ta kuma ce ta shirya tsaf tare da haɗin gwiwar sauran jami’an tsaro wajen dakile duk wani yunkuri na kawo tashin hankali a lokacin zaɓen.