fidelitybank

Akwai yuwar na yi ritaya a Al-Nassr saboda ina jin dadin Saudiyya – Ronaldo

Date:

Tauraron ɗan wasan Portugal da ƙungiyar Al-Nassr ta Saudiyya, Cristiano Ronaldo, ya ce “akwai yiwuwar” ƙungiyar ta zamar masa ta ƙarshe da zai yi ritaya daga murza leda.

Ɗan ƙwallon mai shekara 39 ya koma Saudiyya ne a watan Janairun 2023 bayan ya bar Manchester United, wanda aka sha alaƙantawa da komawa Sporting Lisbon, kulob ɗin da ya fara wasa.

Sai dai ya faɗa wa gidan talabijin na Now cewa: “Ban sani ba ko zan yi ritaya nan gaba kaɗan, cikin shekara biyu ko uku, amma ƙila na yi ritaya a nan Al-Nassr.”

“Ina jin daɗin zama a wannan ƙungiyar, ina jin daɗin ƙasar ma. Ina jin daɗin taka leda a Saudiyya kuma ina so na ci gaba da yin hakan.”

Tsohon ɗan wasan na Real Madrid da Juventus ya ci ƙwallo 898 a tarihin sana’arsa, inda ya ci wa ƙasarsa 130 daga cikinsu kuma yake son ƙarawa a kansu bayan ya tabbatar da cewa ba zai jingine takalmansa ba a yanzu.

“Idan zan bar tawagar Portugal ba zan faɗa wa kowa ba kafin yanke hukuncin, kuma babu tsammani zan yanke shi amma bayan na yi tunani sosai,” in ji shi.

uanguard news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp