Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC, ta ce, bankunan kasuwanci ne suka janyo tarnaƙi wajen ganin sabbin kuɗi sun wadata a hannun jama’a.
EFCC ta ce, bayanai daga Babban Bankin Najeriya sun nuna cewa zuwa yanzu, CBN ya buga sabbin takardun kuɗi sama da naira biliyan 400, amma bankuna sun ƙi fitarwa su bai wa jama’ar ƙasar.
Shugaban hukumar EFCC, Abdurrasheed Bawa a wata tattaunawa da BBC, ya buƙaci ‘yan Najeriya su tona asirin masu ɓoye sabbin kuɗi, don ganin hukumar ta je ta ƙwace su.
Abdurrashe Bawa ya ce wannan ita ce mataki na gaba da suke ganin zai taimaka wajen kawo wa talakan Najeriya waraka.
Sannan ya tunasar da cewa akwai tukuici mai gwabi ga duk mutumin da ya taimaka aka gano wurare ko mutumin da ke rike da sabbin kudade.