fidelitybank

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Date:

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar da ta afku a garin Mokwa da ke jihar Neja wadda ta laƙume rayuka sama da 200, a matsayin “abin takaici, sai dai kaddara ce daga Allah”.

Babangida ya bayyana haka ne lokacin da ya karɓi bakuncin tawagar gwamnatin jihar karkashin jagorancin mataimakin gwamnan jihar Yakubu Garba, da suka kai masa gaisuwar sallah a gidansa da ke Minna, kamar yadda gidan talabijin na Channels ta ruwaito.

Yayin da yake miƙa sakon ta’aziyyarsa ga mutanen Mokwa da ma ɗaukacin al’ummar jihar kan bala’in da ambaliyar ta haddasa, Babangida ya buƙaci da su ci gaba da yi wa waɗanda suka rasu addu’a.

“Abin da ya faru a Mokwa abin takaici ne, sai dai haka Allah ya tsara. Lamari ya fi karfin mu, shi ya sa yana da kyau mu ci gaba da yin addu’a ga mutanen da suka rasu,” in ji IBB.

tribune news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp