Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar da ta afku a garin Mokwa da ke jihar Neja wadda ta laƙume rayuka sama da 200, a matsayin “abin takaici, sai dai kaddara ce daga Allah”.
Babangida ya bayyana haka ne lokacin da ya karɓi bakuncin tawagar gwamnatin jihar karkashin jagorancin mataimakin gwamnan jihar Yakubu Garba, da suka kai masa gaisuwar sallah a gidansa da ke Minna, kamar yadda gidan talabijin na Channels ta ruwaito.
Yayin da yake miƙa sakon ta’aziyyarsa ga mutanen Mokwa da ma ɗaukacin al’ummar jihar kan bala’in da ambaliyar ta haddasa, Babangida ya buƙaci da su ci gaba da yi wa waɗanda suka rasu addu’a.
“Abin da ya faru a Mokwa abin takaici ne, sai dai haka Allah ya tsara. Lamari ya fi karfin mu, shi ya sa yana da kyau mu ci gaba da yin addu’a ga mutanen da suka rasu,” in ji IBB.