Kocin Manchester City, Pep Guardiola ya bayyana kungiyoyi hudu da za su iya lashe gasar zakarun Turai bayan Manchester City ta fitar da ita daga gasar.
Guardiola ya kalli yadda Real Madrid ta fitar da kungiyarsa daga gasar zakarun Turai ranar Laraba.
Kungiyar Guardiola ta sha kashi ne da ci 3-1 a karawar da suka yi a filin wasa na Santiago Bernabeu.
Zakarun gasar Premier sun sha kashi da ci 3-2 a wasan farko a makon jiya a filin wasa na Etihad.
Sun fice gasar ne da jimillar kashi 6-3 a dukkan wasannin biyu.
Da yake magana a wata hira da ya yi bayan wasan bayan kammala wasan, Guardiola ya ce kungiyoyi irinsu Real Madrid, Paris Saint-Germain, Liverpool da Barcelona su ne kungiyoyi hudu da za su iya lashe gasar zakarun Turai a bana.
Sai dai dan kasar Sipaniya, ya yarda cewa kungiyar Carlo Ancelotti ce ta daya da aka fi so a gasar.
“Hakika Madrid ‘yan takara ne, tabbas,” in ji Guardiola.
“Amma akwai wasu kungiyoyi masu kyau a kusa. Zai kasance kakar gasar zakarun Turai mai ban sha’awa.
“Madrid ita ce ke kan gaba wajen wannan kofi. Akwai sauran kungiyoyin da suke da kyau sosai a kakar wasa amma Madrid ta kasance mafi fifiko.
“Amma akwai wasu kungiyoyin da ke taka leda sosai. Liverpool tana cikin kyakkyawan yanayi har zuwa yanzu, Barcelona tana da ban mamaki, Paris Saint-Germain, tare da abokina Luis [Enrique] ne ke jagorantar tafiya.
“Amma a fili, Madrid sun fi so.”