Majalisar dattawa ta ce, akwai jan aiki a gaban gwamnati wajen kawar da yunwa a ƙasar bisa la’akari da kasafin kuɗin da aka ware wa harkokin noma a bana.
Kwamtitin majalisar mai kula da noma da raya karkara ne ya bayyana damuwa a kan rage kuɗin da za a kashe wa harkar noma a cikin kasafin 2025.
Gwamnati dai ta keɓe wa ɓangaren noma naira billiyan ɗari takwas da ashirin da shida wato kashi 1.7 na kasafin kuɗin na bana ne.
Sanata Salihu Mustapha shi ne shugaban kwamitin noma a majalisar, ya bayyana cewa wannan kasafin da aka ware ya yi kaɗan domin bunƙasa ɓangaren.