fidelitybank

Akwa Ibom: An rufe dakunan gwaje-gwaje 12 marasa inganci

Date:

Akalla dakunan gwaje-gwaje 12 ne ma’aikatar lafiya ta jihar Akwa Ibom ta rufe da hadin gwiwar kungiyar kula da dakunan gwaje-gwajen kiwon lafiya ta kasa (LSCN).

Da ya ke zantawa da manema labarai a Uyo a karshen mako, jim kadan bayan tawagar sa ido ta rufe dakunan gwaje-gwajen, kwamishinan lafiya, Farfesa Augustine Umoh, ya ce aikin ya bi umarnin majalisar zartarwa ta jihar kan rashin ingancin ayyukan kiwon lafiya da a ke samu a jihar.

Kwamishinan ya ayyana laifukan da su ka shafi dakunan gwaje-gwajen da su ka hada da rashin takardar shedar rijista da ma’aikatar lafiya ta jihar da rashin shaidar yin rijista da majalisar dakin gwaje-gwajen na likitoci ta Najeriya da rashin kwararrun masana kimiyyar dakin gwaje-gwaje da sauran ma’aikatan da su ka taimaka a dakin binciken.

Sauran laifuffukan sun hada da rashin daidaitaccen ɗan littafin sakamakon gwaji, babu samar da rijistar dakin gwaje-gwaje da rashin lasisin aiki na masu fasahar dakin gwaje-gwaje da kuma ayyuka marasa ɗa’a da haɗari.

Ya ce, “Na samu korafe-korafe da dama dangane da wuraren dakunan gwaje-gwajen likitoci da ayyukan da a ke yi kuma aikin wani yunkuri ne na gyara wasu daga cikin abubuwan da ba su dace ba.

“A gaskiya, Majalisar zartaswar jihar da ta samu da yawa daga cikin wadannan rahotanni ita ma ta ba da umarnin a gudanar da wannan aikin . Domin haka manufarmu ita ce mu yi amfani da wannan aikin, domin ba da ƙarin umarni ga aikin idan ayyukan dakin gwaje-gwaje a cikin jihar. ” Inji Farfesa Agustine.

Kwamishinan ya bayyana cewa sa idon, za a fadada dakunan gwaje-gwaje har zuwa sauran sassan jihar.

opra news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...

Bajintar ɗaliban Najeriya a gasar Turanci ta nuna ingancin ilimi a ƙasa – Tinubu

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, ya taya ƴanmatan nan uku...

Ƙudirin faɗaɗa mamayar Gaza zai ƙara jefa Falasɗinawa cikin hatsari – MDD

Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana rahotannin da ke kwarmata...

APC a Kano mu na jinjinawa Tinubu – Abdullahi Abbas

Shugabannin jam’iyyar APC a jihar Kano, sun yabawa shugaba...

Kwamishinan da ake tuhuma da belin dilan kwayoyi a Kano ya yi murabus

Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi ya...

Turji ya saki Mutane 32 bayan zaman sulhu

Shahararren shugaban ‘yan bindiga, Bello Turji, ya saki mutane...

ADC ta gargadi El’Rufa’i kan ruguza jam’iyyar

Shugaban jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a jihar Kaduna,...

An gindayawa Thomas Partey sharudan beli

An gindaya sharuddan belin tsohon dan wasan tsakiya na...

Fursunoni 37 na jiran zartas musu da hukuncin kisa a Bauchi

Fursunoni 37 da aka yanke wa hukuncin kisa bisa...

Kwamitin sulhu na MDD zai gana kan makomar ƴan Isra’ila da ke hannun Hamas

Kwamitin tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya zai tattauna yau...
X whatsapp