fidelitybank

Akwa Ibom: An rufe dakunan gwaje-gwaje 12 marasa inganci

Date:

Akalla dakunan gwaje-gwaje 12 ne ma’aikatar lafiya ta jihar Akwa Ibom ta rufe da hadin gwiwar kungiyar kula da dakunan gwaje-gwajen kiwon lafiya ta kasa (LSCN).

Da ya ke zantawa da manema labarai a Uyo a karshen mako, jim kadan bayan tawagar sa ido ta rufe dakunan gwaje-gwajen, kwamishinan lafiya, Farfesa Augustine Umoh, ya ce aikin ya bi umarnin majalisar zartarwa ta jihar kan rashin ingancin ayyukan kiwon lafiya da a ke samu a jihar.

Kwamishinan ya ayyana laifukan da su ka shafi dakunan gwaje-gwajen da su ka hada da rashin takardar shedar rijista da ma’aikatar lafiya ta jihar da rashin shaidar yin rijista da majalisar dakin gwaje-gwajen na likitoci ta Najeriya da rashin kwararrun masana kimiyyar dakin gwaje-gwaje da sauran ma’aikatan da su ka taimaka a dakin binciken.

Sauran laifuffukan sun hada da rashin daidaitaccen ɗan littafin sakamakon gwaji, babu samar da rijistar dakin gwaje-gwaje da rashin lasisin aiki na masu fasahar dakin gwaje-gwaje da kuma ayyuka marasa ɗa’a da haɗari.

Ya ce, “Na samu korafe-korafe da dama dangane da wuraren dakunan gwaje-gwajen likitoci da ayyukan da a ke yi kuma aikin wani yunkuri ne na gyara wasu daga cikin abubuwan da ba su dace ba.

“A gaskiya, Majalisar zartaswar jihar da ta samu da yawa daga cikin wadannan rahotanni ita ma ta ba da umarnin a gudanar da wannan aikin . Domin haka manufarmu ita ce mu yi amfani da wannan aikin, domin ba da ƙarin umarni ga aikin idan ayyukan dakin gwaje-gwaje a cikin jihar. ” Inji Farfesa Agustine.

Kwamishinan ya bayyana cewa sa idon, za a fadada dakunan gwaje-gwaje har zuwa sauran sassan jihar.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp