Akalla dakunan gwaje-gwaje 12 ne ma’aikatar lafiya ta jihar Akwa Ibom ta rufe da hadin gwiwar kungiyar kula da dakunan gwaje-gwajen kiwon lafiya ta kasa (LSCN).
Da ya ke zantawa da manema labarai a Uyo a karshen mako, jim kadan bayan tawagar sa ido ta rufe dakunan gwaje-gwajen, kwamishinan lafiya, Farfesa Augustine Umoh, ya ce aikin ya bi umarnin majalisar zartarwa ta jihar kan rashin ingancin ayyukan kiwon lafiya da a ke samu a jihar.
Kwamishinan ya ayyana laifukan da su ka shafi dakunan gwaje-gwajen da su ka hada da rashin takardar shedar rijista da ma’aikatar lafiya ta jihar da rashin shaidar yin rijista da majalisar dakin gwaje-gwajen na likitoci ta Najeriya da rashin kwararrun masana kimiyyar dakin gwaje-gwaje da sauran ma’aikatan da su ka taimaka a dakin binciken.
Sauran laifuffukan sun hada da rashin daidaitaccen ɗan littafin sakamakon gwaji, babu samar da rijistar dakin gwaje-gwaje da rashin lasisin aiki na masu fasahar dakin gwaje-gwaje da kuma ayyuka marasa ɗa’a da haɗari.
Ya ce, “Na samu korafe-korafe da dama dangane da wuraren dakunan gwaje-gwajen likitoci da ayyukan da a ke yi kuma aikin wani yunkuri ne na gyara wasu daga cikin abubuwan da ba su dace ba.
“A gaskiya, Majalisar zartaswar jihar da ta samu da yawa daga cikin wadannan rahotanni ita ma ta ba da umarnin a gudanar da wannan aikin . Domin haka manufarmu ita ce mu yi amfani da wannan aikin, domin ba da ƙarin umarni ga aikin idan ayyukan dakin gwaje-gwaje a cikin jihar. ” Inji Farfesa Agustine.
Kwamishinan ya bayyana cewa sa idon, za a fadada dakunan gwaje-gwaje har zuwa sauran sassan jihar.