fidelitybank

Akwai fargabar mutuwar mutane 20 a jihar Kogi

Date:

Mutane fiye da 20 ne ake ba da rahotannin cewa, sun mutu sanadin gobara lokacin da kan wata tankar man fetur ta kwace saboda bayan shanyewar burki.

Lamarin dai ya kuma janyo ruftawar gadar Kogin Maboro a cikin karamar hukumar Ankpa ta jihar Kogi. Jaridar Daily Trust ta ruwaito wani shaida yana cewa lamarin ya faru ne cikin tsakar dare da misalin karfe 3:30.

Shaidan ya ce lamarin shi ne babban iftila’i na biyu da ya faru a Ankpa cikin wannan wata, sai dai na daren Laraba ya fi muni da tayar da hankula.

A cewarsa fiye da mutum 20 ne suka kone, wasu ma kurmus ba za a iya tantance ko su wane ne ba.

Ya ce sassan jikin mutanen da suka rasu sun yi kaca-kaca a fadin wurin da gobarar ta tashi. In ji shi, sai da aka yi amfani da buhuna don zuba sassan jikin da suka kone.

Kwamandan Hukumar Kiyaye Hadurra ta Kasa reshen jihar Kogi, Stephen Dawulung ya tabbatar da faruwar lamarin amma ya ce ba zai iya tabbatar da ko mutane nawa ne gobarar ta shafa ba tukunna.

www.legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp