fidelitybank

Akwai dalilin da ya sa za mu binciki gwamnatin Buhari – Majalisa

Date:

Majalisar Dattija ta bayyana dalilan da ya sa ta yanke shawarar binciken tsohuwar gwamnatin Buhari.

A zaman da ta yi ranar Talata ne majalisar ta tsayar da shawarar gudanar da bincike kan yadda tsohuwar gwamnatin ta kashe wasu kudi da suka kai tiriliyan 30 da ta karba daga Babban Bankin kasa CBN.

Sanata Ali Ndume daga Jihar Borno kuma mai tsawatarwa na Majalisar Dattijan, ya ce Æ´an majalisar na da damar yin bincike, kuma a cewarsa ” binciken zai soma ne daga CBN”

Ya kuma ce binciken na iya faÉ—aÉ—a ya kai har inda ba a yi tsammani ba.

Sanata Ndume ya ce za su bibiyi bayanai na wadanda aka ba kuÉ—in da kuma yadda aka kashe su da abin da aka yi da kudaden.

Ya ce binciken zai iya wuce tunanin mutane na za a binciki gwamnatin Buhari, “wataÆ™ila abin ya wuce inda ake tsammani, kawai dai ba mu sani ba sai an yi binciken za a gane,” in ji shi.

Kuɗaɗen dai na bashi ne da Babban Bankin Najeriya ya ba gwamnati domin gudanar da ayyuka ko biyan wasu buƙatu.

Sanata Ndume ya ce sai bayan an karɓo kuɗaɗen kafin gwamnatin ta gabatar wa majalisa domin neman amincewarta, wanda ya ce ba ta da hurumi.

“Kundin tsarin mulki ya ba mu dama ne mu amince da abin da za a yi ba abin da aka riga aka yi ba,” in ji Sanata Ndume.

Majalisar dattijan ta yi iÆ™irarin cewa fitar da kuÉ—aÉ—en da su ba bisa Æ™a’ida ba Æ™arkashin jagorancin tsohon shugaban Babban Bankin Godwin Emefiele ne ya jefa Æ™asar cikin Æ™arancin abinci da ta ke fuskanta.

Majalisar ta cimma matsayar kafa kwamitin da zai gudanar da bincike kan yadda aka kashe kudaden da ba a ba majalisar damar sanin haƙiƙanin yadda bayanan yadda aka kashe su ba.

Kwamitin zai kuma binciki naira tiliyan 10 na shirin tallafa wa manoma na Anchor Borrowers da kuma dala biliyan 2.4 daga dala biliyan bakwai na sauran shirye-shiryen gwamnati na tallafi.

@nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp