Dakarun sojoji karkashin Operation Hadin Kai a Jihar Borno sun kwato akuyoyi guda 500 daga mambobin kungiyar Islamic State West Africa Province (ISWAP) a karamar hukumar Jere, Jihar Borno.
Daily Trust ta ce, an kashe wasu da ake zargi ‘yan ISWAP ne yayin musayar wuta tsakanin sojojin da barayin akuyoyin, wanda hakan ya yi sanadiyar mutuwar wasu daga cikin barayin.
Wata majiya, ta ce masu kiwon dabobin sun aike da sakon a zo a cece su zuwa ga kwamandan Operation Lafiya Dole, Manjo Janar Chris Musa, inda suka sanar da shi satar dabobin da aka yi musu.
“Sojojin sun bi sahun barayin dabobin suka tare su a wani wuri kusa da fitaccen gonar Kashu suka yi musayar wuta da su har sai da suka kashe biyar har lahira yayin da sauran suka tsere suka bar akuyoyin su,” a cewar majiyar ta tsaro.