fidelitybank

Akpabio ya garzaya wajen Tinubu a kan tantance Keyamo

Date:

Rahotanni daga fadar Shugaba kasa na cewa, Shugaban Majalisar Dattijai Godswill Akpabio, ya garzaya fadar shugaban ƙasa ɗazu da rana.

Jaridu sun ruwaito cewa an ga Akpabio a fadar shugaban ƙasa ne da misalin 2:55 na rana.

Babu cikakkun bayanai kawo yanzu a kan dalilan ziyarar tasa zuwa fadar Aso Rock.

Sai dai ziyarar ta zo ne bayan majalisar dattijan ta shiga zaman sirri a kan hargowar da ta ɓarke a zauren majalisar lokacin da ake ƙoƙarin tantance Festus Keyamo a matsayin minista.

Kan ƴan majalisar dai ya rabu biyu ne a kan ko su dakatar da tantance Keyamo, saboda zargin raina majalisa da kiran ƴan majalisar gurɓatattun mutane lokacin da yake minista zamanin gwamnatin Shugaba Buhari.

An shafe tsawon lokaci ana hayaniya a majalisar kafin daga baya ƴan majaliasar dattijan su amince su shiga ganawar sirri don warware matsalar.

Daga nan ne aka nemi ƴan jarida tare da Festus Kiyamo su fita daga zauren.

vgn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp