Shugaban Majalisar Dattija Sanata Godswill Akpabio, ya sanar da Opeyemi Bamidele a matsayin, shugaban masu rinjaye na majalisar dattijai.
Ya bayyana haka ne yayin zaman majalisar na ranar Talata, inda ya bayyana Sanata David Umahi a matsayin mataimakin shugaban masu rinjaye.
Haka zalika ya ce rukunin ‘yan majalisar dattijai na jam’iyyar APC mai mulki sun amince da Mohammed Ali Ndume, a matsayin mai tsawatarwa na É“angaren masu rinjaye a majalisar.
Sai kuma Sanata Oyelola Yisa Ashiru matsayin mataimakin mai tsawatarwa na ɓangaren masu rinjaye.
Jim kaÉ—an kuma haka ne, sai aka sanar da Sanata Simon Mwadkon Davou a matsayin shugaban marasa rinjaye, yayin da Oyewumi Olalere ya kasance mataimakin shugaban marasa rinjaye.
Haka zalika, an zaÉ“i Sanata Darlington Nwokocha, a muÆ™amin mai tsawatarwa na É“angaren marasa rinjaye, sai Sanata Rufa’i Sani Hanga, mataimakin mai tsawatarwa na É“angaren marasa rinjaye a majalisar dattijai.