Dan takarar jam’iyyar APC a zaɓen gwamnan jihar Ondo, Lucky Aiyedatiwa na gaba gaba a sakamakon da aka fitar kawo yanzu.
Hukumar zaɓen ƙasar ta karɓi sakamakon zaɓen daga ƙananan hukumomi 15 cikin 18 na jihar, inda kuma a jam’iyyar APC ke kan gaba a duka ƙananan hukumomin da aka tattara, sai kuma PDP ke biye.
Ɗan takarar na APC ya samu ƙuri’a 301,113, yayin da ɗan takarar PDP ya samu ƙuri’a 97,051.