fidelitybank

Aisha Buhari ta sanya Zamfara a cikin addu’o’in ta

Date:

Uwargidan shugaban kasa, Aisha Muhammadu Buhari, ta wallafa wani sako a shafinta na Facebook, inda a ciki ta yi wa al’ummar jihar Zamfara ta addu’ar zaman lafiya.

Aisha Buhari ta wallafa sakon ne da misalin karfe 12:09 na daren Laraba, inda ta roki Allah ya samar wa mutanen jihar – har da sauran ‘yan kasar – mafita daga matsalar tsaron da ta addabe ta, musamman a lokacin da Musulmi ke raya dare domin neman falalar Lailatul Kadri:

“Allah ya fitar da mu da mutanen jihar Zamfara daga chikin wannan hali, albarkacin daren Lailatul Kadri, Ameen!”

Baya ga sakon, uwargidan shugaban Najeriyar ta kuma wallafa wani sako na sauti mai tsawon minti 3:53, wanda a ciki ana iya jin wani mutumin da bai fadi sunansa ba yana sanar da wani mutumin da ya kira ‘Haji Abdurrahman’ labarin wani kamun da ‘yan sa-kai suka yi wa wasu barayin daji a yankin Tsafe da Mada na jihar Zamfara.

A farkon sautin ana iya jin muryar wata mata da ke cewa, “Ga shi ku ji me yake fada…” Sai dai ba mu san ko muryar ta uwargidan shugaba Buhari ba ce.

hausa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...
X whatsapp