fidelitybank

Aisha Buhari ta baiwa Kashim Shettima muƙami a Kwalejin Future Assured

Date:

 

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Aisha Buhari, ta naɗa Kashim Shettima, tsohon gwamnan Jihar Borno, a matsayin shugaban kwamitin amintattu na Kwalejin Future Assured da ke Maiduguri.

Gidauniyar Aisha Buhari Foundation ce ta gina kwalejin a Maiduguri domin daukar nauyin karatun wadanda rikicin Boko Haram ya shafa a jihar.

Yayin kaddamar da kwamitin gudanarwa na kwalejin mai mambobi 11 karkashin jagorancin Shettima a fadar shugaban kasa da ke Abuja a ranar Talata, Aisha Buhari ta hori mambobin da su dage wajen sauke nauyin tare da sadaukarwa wajen gudanar da makarantar.

Ta ce “Na zabe ku a tsanake a matsayin mambobin kwamitin da za ku kula da harkokin gudanarwar kwalejin. Aikin na da girma, amma na yi imani za ku iya daukar nauyin.

“Saboda haka, ina addu’a cewa dukkanmu mu hada kai don cimma burinmu na saka jari a ‘ya’yanmu, mu tabbatar da makomarsu da kuma bunkasa al’umma ta hanyar yi wa bil’adama hidima.”

Ta baiyana godiya ga gwamnati da al’ummar Borno bisa goyon baya da hadin kai.

Aisha Buhari ta kuma godewa gidauniyar TY Danjuma da sauran ƙungiyoyi da suka bayar domin samun nasarar aikin.

A jawabinsa na karbar muƙamin, Shettima ya baiyana godiyarsa ga uwargidan shugaban kasar da ta ga cancantarsa ga muƙamin.

Ya bayyana kudurinsa na ganin an aiwatar da aikin ta hanyar tabbatar da cewa an kiyaye ka’idojin makarantar domin amfanin marayu.

Sauran wadanda aka nada a kwamitin sun hada da Halima Buhari-Sherrif a matsayin Sakatariya, Dr Muhammad Idris, Hadi Uba, Muhammad Albishir, Farfesa Bulama Kagu, Farfesa Aisha Ahmed, Asabe Vilita-Bashir, Dr Hajo Sani, Nana Liberty da Hauwa Ngoma.

nan news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp