Uwargidan Shugaban Ƙasa, Aisha Buhari, ta naɗa Kashim Shettima, tsohon gwamnan Jihar Borno, a matsayin shugaban kwamitin amintattu na Kwalejin Future Assured da ke Maiduguri.
Gidauniyar Aisha Buhari Foundation ce ta gina kwalejin a Maiduguri domin daukar nauyin karatun wadanda rikicin Boko Haram ya shafa a jihar.
Yayin kaddamar da kwamitin gudanarwa na kwalejin mai mambobi 11 karkashin jagorancin Shettima a fadar shugaban kasa da ke Abuja a ranar Talata, Aisha Buhari ta hori mambobin da su dage wajen sauke nauyin tare da sadaukarwa wajen gudanar da makarantar.
Ta ce “Na zabe ku a tsanake a matsayin mambobin kwamitin da za ku kula da harkokin gudanarwar kwalejin. Aikin na da girma, amma na yi imani za ku iya daukar nauyin.
“Saboda haka, ina addu’a cewa dukkanmu mu hada kai don cimma burinmu na saka jari a ‘ya’yanmu, mu tabbatar da makomarsu da kuma bunkasa al’umma ta hanyar yi wa bil’adama hidima.”
Ta baiyana godiya ga gwamnati da al’ummar Borno bisa goyon baya da hadin kai.
Aisha Buhari ta kuma godewa gidauniyar TY Danjuma da sauran ƙungiyoyi da suka bayar domin samun nasarar aikin.
A jawabinsa na karbar muƙamin, Shettima ya baiyana godiyarsa ga uwargidan shugaban kasar da ta ga cancantarsa ga muƙamin.
Ya bayyana kudurinsa na ganin an aiwatar da aikin ta hanyar tabbatar da cewa an kiyaye ka’idojin makarantar domin amfanin marayu.
Sauran wadanda aka nada a kwamitin sun hada da Halima Buhari-Sherrif a matsayin Sakatariya, Dr Muhammad Idris, Hadi Uba, Muhammad Albishir, Farfesa Bulama Kagu, Farfesa Aisha Ahmed, Asabe Vilita-Bashir, Dr Hajo Sani, Nana Liberty da Hauwa Ngoma.