fidelitybank

Aikin Hajjin shekarar 2024 ka iya kai wa kusan miliyan 5 – NAHCON

Date:

Hukumar kula da Alhazai ta ƙasa, ta shawarci maniyyata aikin hajjin shekara mai mai zuwa ta 2024, su ajiye naira miliyan huɗu da rabi a matsayin adashin gata, kafin lokacin da za a fito da hakikanin kuɗin hajjin shekarar.

Hukumar ta ce hakan ya faru ne sakamakon tashin farashin dala wadda da ita ne ake yin kiyasin dukkanin abubuwan da maniyyata suke bukata.

Kwamishinan kuɗi da tsare-tsare na hukumar Alhaji Nura Hassan Yakasai ya shaida wa BBC cewa matakin na zuwa ne bayan da suka yi la’akari da tashin farashin dala.

Ya ce wannan shi ne dalilin da ya sa hukumar ta yanke shawar ajiye naira miliyan 4.5 a matsayin adashin gata, “idan akwai ciko ma ba zai yi yawa ba”.

Ya ƙara da cewa “Kashi 98 na kuɗaɗen da ake buƙata wajen biyan aikin hajji ana yi ne da dala” dan haka ne suka ɗauki matakin shawartar maniyya su biya wannan kuɗi a matsayin adashin gata.

Ya ce dalilin da ya sa hukumar ta yanke wanna shawarar shi ne kada cikon ya yi wa maniyyata yawa a lokacin biyan kudin aikin hajjin. In ji BBC.

dailypost news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp