Shugaban kasar Algeria ya ce, zai ɓullo da sabon tsarin biyan matasan da ba su da aikin yi a ƙasar yayin da take fama da adadin marasa aikin.
Shugaba Abdelmadjid Tebboune ya faɗa wa ‘yan jarida cewa, za a fara biyan matasan ‘yan shekara 19 zuwa 40 daga watan Maris.
Waɗanda suka cancanci shiga tsarin za su karɓi kuɗin da ya kai kusan dala 100 duk wata, da kuma wasu tallafi na lafiya, har sai sun samu aikin yi.
Da yake ba da sanarwar, Tebboune ya ce, “Algeria ce ƙasa ta farko da ta fito da irin wannan shirin wanda ba ta Turai ba. Akwai marasa aikin yi 600,000 a ƙasar”. a cewarsa in ji BBC.