Shugaban Majalisar Dattawa, Dakta Ahmad Ibrahim Lawan, ya yi watsi da alkawarin da ya yi a baya na cewa ba zai daukaka kara ba kan tikitin takarar Sanatan Yobe ta Arewa da ya sha kaye a hannun Bachir Machina.
An gudanar da zaben fidda gwani na Sanatan Yobe ta Arewa a ranar 28 ga watan Mayun 2022 a daidai lokacin, Lawan ya tsaya takarar neman tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress, APC a 2023, wanda ya sha kaye a hannun Asiwaju Bola Tinubu.
A ranar Litinin din da ta gabata ne, takardun kotun mai lamba FHC/DM/CS/11/2022 da wakilin DAILY POST ya gani ya nuna cewa jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na kalubalantar hukuncin da babbar kotun tarayya da kotun daukaka kara suka yanke na tabbatar da takarar Machina.
Karanta Wannan:Â Ba ni da niyyar daukaka kara a kan hukuncin kotu – Ahmed Lawan
Daga daukaka karar, Lawan na neman izinin kotun koli ta ajiye hukuncin da kotunan daukaka kara ta yanke tare da bayyana shi a matsayin wanda ya yi nasara.
Kotun koli ta sanya ranar 1 ga watan Fabrairu za a fara sauraron karar.