Mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo a ranar Litinin ya kalubalanci Afirka da ta samar da abin da take ci tare da rage dogaro da kasashen waje.
Osinbajo ya yi wannan kiran ne a wajen wani taron shuwagabanni da shugabannin majalisun kasashen Afrika da aka gudanar a Abuja.
Ya ce cutar ta COVID-19, alal misali, ta haifar da karancin abinci a Afirka, yana mai jaddada cewa, akwai bukatar Afirka ta samu dogaro da kanta wajen samar da abinci.
Osinbajo ya kuma jaddada cewa, dole ne Afirka ta samar da abin da take ci, yana mai cewa, akwai bukatar kara hadin gwiwa wajen tunkarar al’amura a Afirka.