Majalisar Dokokin Afirka ta Kudu ta yanke hukuncin rufe ofishin jakadancin Isra’ila da ke birnin Pretoria tare da dakatar da duk wata hulɗar diplomasiyya tsakaninta da ƙasar.
Majalisar ta ɗauki matakin ne har sai Isra’ila ta amince da yarjejeniyar tsagaita wuta a Zirin Gaza tare da hawa teburin sasantawa.
Jami’iyar ANC mai mulki, wadda take da rinjaye a majalisar dokokin ƙasar, ta kwatanta gwagwamayar Falasɗinawa da irin wadda Afirka ta Kudu ta sha lokacin da suke fafutikar neman ƴancin kai daga fararen fata.
Wakilin BBC ya ce gabanin kaɗa ƙuri’ar, Isra’ila ta yi wa jakadanta kiranye, inda ta ce za ta tattauna da shi .