fidelitybank

Afrika ta Kudu ta kama Fasto dan Najeriya da zargin yin fyade

Date:

An sake kama wani fasto ɗan Najeriya da aka wanke kan zargin aikata fyaɗe, a cewar ƴansandan Afirka ta Kudu.

Ƴansandan sun ce an kama faston ne a ranar Asabar, sai dai a yanzu ana zarginsa da laifuka da suka shafi shige da fice.

An sake Timothy Omotoso ne a watan da ya gabata, bayan zama a gidan yari na tsawon shekaru tara yana jiran shari’a kan laifin fyaɗe da kuma cin zarafin lalata da wasu ƴan mata daga cocinsa.

Wanke shi da aka yi – ya janyo fushi a faɗin Afirka ta Kudu.

Duk da cewa maganganun faston ba lallai su zama gaskiya ba, masu gabatar da ƙara sun yi kuskure wajen gudanar da shari’ar da ake yi masa, a cewar alkalin da ya jagoranci shari’ar.

Hukumomin shige da fice da kuma ƴansanda sun kama Omotoso ne a garin East London a safiyar Asabar, jim kaɗan bayan kammala ibada a cocinsa, kamar yadda kwamishinan ƴansandan lardin ya faɗa wa manema labarai.

“Zai fuskanci tuhuma da ta shafi saɓa wa dokar shige da fice, kuma zai gurfana gaban kotu ranar Litinin,” in ji ƴansanda.

nigerian 
news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp