An sake kama wani fasto ɗan Najeriya da aka wanke kan zargin aikata fyaɗe, a cewar ƴansandan Afirka ta Kudu.
Ƴansandan sun ce an kama faston ne a ranar Asabar, sai dai a yanzu ana zarginsa da laifuka da suka shafi shige da fice.
An sake Timothy Omotoso ne a watan da ya gabata, bayan zama a gidan yari na tsawon shekaru tara yana jiran shari’a kan laifin fyaɗe da kuma cin zarafin lalata da wasu ƴan mata daga cocinsa.
Wanke shi da aka yi – ya janyo fushi a faɗin Afirka ta Kudu.
Duk da cewa maganganun faston ba lallai su zama gaskiya ba, masu gabatar da ƙara sun yi kuskure wajen gudanar da shari’ar da ake yi masa, a cewar alkalin da ya jagoranci shari’ar.
Hukumomin shige da fice da kuma ƴansanda sun kama Omotoso ne a garin East London a safiyar Asabar, jim kaɗan bayan kammala ibada a cocinsa, kamar yadda kwamishinan ƴansandan lardin ya faɗa wa manema labarai.
“Zai fuskanci tuhuma da ta shafi saɓa wa dokar shige da fice, kuma zai gurfana gaban kotu ranar Litinin,” in ji ƴansanda.