fidelitybank

Afrika ta Kudu ta kama Fasto dan Najeriya da zargin yin fyade

Date:

An sake kama wani fasto ɗan Najeriya da aka wanke kan zargin aikata fyaɗe, a cewar ƴansandan Afirka ta Kudu.

Ƴansandan sun ce an kama faston ne a ranar Asabar, sai dai a yanzu ana zarginsa da laifuka da suka shafi shige da fice.

An sake Timothy Omotoso ne a watan da ya gabata, bayan zama a gidan yari na tsawon shekaru tara yana jiran shari’a kan laifin fyaɗe da kuma cin zarafin lalata da wasu ƴan mata daga cocinsa.

Wanke shi da aka yi – ya janyo fushi a faɗin Afirka ta Kudu.

Duk da cewa maganganun faston ba lallai su zama gaskiya ba, masu gabatar da ƙara sun yi kuskure wajen gudanar da shari’ar da ake yi masa, a cewar alkalin da ya jagoranci shari’ar.

Hukumomin shige da fice da kuma ƴansanda sun kama Omotoso ne a garin East London a safiyar Asabar, jim kaɗan bayan kammala ibada a cocinsa, kamar yadda kwamishinan ƴansandan lardin ya faɗa wa manema labarai.

“Zai fuskanci tuhuma da ta shafi saɓa wa dokar shige da fice, kuma zai gurfana gaban kotu ranar Litinin,” in ji ƴansanda.

leadership newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Majalisar Dinkin Duniya za ta dakatar da tallafin abinci a Najeriya

Shirin Abinci na Majalisar Ɗinkin Duniya (WFP) ya bayyana...

Tinubu ya na murkushe ‘Yan adawa – Sule Lamido

Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya ce...

Gwamnatin Kano ta baiwa yara fifiko – UNICEF

Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya...

Majalisar ta amince da buƙatar Tinubu na ciyo bashin dala biliyan 21

A ranar Talata ne majalisar Dattawa ta amince da...

An sallami Gwamnan Katsina daga asibiti bayan ya samu rauni a hatsarin mota

An sallami gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda,...

Har yanzu Tinubu bai nada Jakadun Najeriya ba – ADC

Jam’iyyar ADC ta soki yadda gwamnatin APC ta shugaba...

Har yanzu ina LP kuma ni ne zan iya saita Najeriya – Datti

Datti Baba-Ahmed, tsohon dan takarar mataimakin shugaban kasa a...

APC ta zama buhun kusa ta gaza a Najeriya – Amaechi

Tsohon gwamnan jihar Ribas, Chibuike Amaechi ya bayyana jam'iyyar...

An fara samun takun saka tsakanin Turkiyya da Najeriya a kan kungiyar Gulen

Kungiyar kare hakkin musulmi, MURIC, ta bukaci shugaban kasar...

Arziƙin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 a farkon 2025 – NBS

Tattalin arzikin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 cikin...

Kamfanonin lantarki za su katse wutar lantarki saboda bashi

Kamfanonin samar da wutar lantarki, sun ce suna iya...

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...
X whatsapp